top of page
Search

Kotun ɗaukaka ƙara ta mayar wa Gwamna Sule na Nasarawa nasararsa ABDULLAHI SULE

  • Writer: Mufkufam
    Mufkufam
  • Nov 23, 2023
  • 1 min read

Gwamnan jihar Nasarawa



Kotun ɗaukaka ƙara da ke zaman ta a Abuja ta yi watsi da hukuncin kotun sauraron ƙorafin zaɓen jihar Nasarawa, inda ta mayar wa Gwamna Abdullahi Sule nasara kamar yadda hukumar INEC ta bayyana a lokacin zaɓen gwamnan jihar na 2023.




A hukuncin da kotun ta yanke yau Alhamis, alƙalan kotun sun bayyana cewa kotun sauraron ƙorafin zaɓen gwamnan jihar Nasarawa ta yi kuskure a hukuncin da ta yanke.

A watan da ya gabata ne dai kotun sauraron ƙorafin zaɓen jihar Nassarawa ta soke nasarar gwamna Abdullahi Sule na jam'iyyar APC, tare da bayyana David Ombugadu na PDP a matsayin wanda ya lashe zaɓen na watan Maris ɗin 2023.

 
 
 

Comments


Post: Blog2_Post

©2023 by Mufkufam. Proudly created with Wix.com

  • Facebook
  • Twitter
  • LinkedIn
bottom of page